Yadda Ake Alwala da Kuma Sallah Irinta Manzon Allah S.A.W a Aikace ATIOSA

 

Alwala da Sallah


ACIGABA DA AYYUKAN ALKHAIRI


YAU LARABA 12/09/1443 DAI-DAI DA 13/04/2022 KUNGIYAR

TSOFAFFIN DALIBAN MAKARANTAR ATIKU AUWAL ISLLAMIYYA ATIOSA. KARKASHIN JAGORANCIN HAZIKIN JAGORA SHUGABAN KUNGIYAR MAL, Uthman Muhammad.


 TA GABATAR DA YANDAAKEYIN  ALWALA DA KUMA YANDA AKEYIN  SALLAH KAMAR YANDA ANNABI YA KOYAR


DAGA CIKIN MALAMAN DA SUKA KARANTAR DA DALIBAN 


  • Ustaz Ibrahim Said
  • Comd Mubarak Umar


USTAZ USMAN_MUHAMMAD_KABIR YA KARANTAR DA YANDA AKEYIN ALWALA 



COMR Saeed Suleiman YA KARANTAR DA YANDA AKEYIN SALLAH



YADDA AKE YIN ALWALA A AIKACE

SALLAH bata yiwuwa saida alwala kuma tilas alwalar ta zamanto anyi

ta da ruwa mai tsarki wanda shine: ruwanda bai canja daga asalin

kamanninsa na ruwa ba,kamar ruwan kogi ko na rijiya ko na idaniyar

ruwa ko na korama.

A KULA DA KYAU:Komai kankantar najasa takan lalata ruwan da yake

dan kadan,amma idan yana da yawa to najasa bata lalata shi har sai

idan ta canja masa kala ko dandano ko kuma kamshi.

1. Ana fara alwala da sunan Allah (Bisimillah) kuma an so a fara da

wanke tafukan hannu a kuma tabbatar sun fita,za ayi hakan sau

uku,musamman ga wanda ya farka daga barci.

A ƘULA DA KYAU:Ba a son a wanke wata gaba sama da sau uku

wannan makaruhi ne.

2. Sannan sai kuskurar baki,tilas ne ayi kuskura na farko,amma idan

aka yi sau uku to shi yafi soyuwa kuma yafi falala.

A KULA DA KYAU: Zuba ruwa a baki kadai baya wadatarwa,dolene sai

an kurkura shi acikin bakin.kuma anso mutum yayi asuwaki yayin

kuskure bakin.

3. Sannan sai shaka ruwa a hanci,tilas ne ayi sau daya a kalla,amma

idan anyi sau uku shi yafi falala.

A KULA DA KYAU: Itama shakar hanci ba wai kawai za'a shigar da

ruwa hanci bane,dole ne ya zamo ta hanyar shakar ruwa tare da

numfashi,kuma ya shigar har cikin hancin sannan ya fyato shi ya fito

tare da numfashi.

4. Sannan sai wanke fuska,itama tilas ne ayi sau daya a kalla,amma

idan anyi sau 3 shi yafi.Za a wanke ta ne tun daga kunnen dama zuwa

na hagu,wannan a kwance kenan,a tsaye kuma tun daga karshen haba

har yazuwa mabubbugar gashin kai.

A KULA DA KYAU: Idan gemun mutum yana da yawa to an so ya

tsefe shi,amma idan bashi da yawa to tilas ne ya tsefe shi ta yadda

ruwa zai ratsa shi.

5. Sannan sai wanke hannaye tun daga 'yan yatsu har zuwa guiwar

hannu,tilas ayi na farko amma idan an kara zuwa sau uku wannan shi

yafi.

A KULA DA KYAU:Ana so a fara da hannun dama kafin na hagu,da

kuma cuccudasu.

6. Sannan sai shafar kai baki dayansa,mutum zai shigar da yan

yatsunsa guda biyu manuniya (sabbaba) cikin kofofin kunnuwansa,sannan

ya shafi fatun kunnuwansa da manyan yan yatsun nasa (ibham)

A KULA DA KYAU:Inda ya wajaba a shafa akai shine:daga mafarin

fuska zuwa kewa,da juyo dashi daga keya zuwa mafarin fuska.kuma

idan gashi yana da yawa ba lallene sai an shafi wanda ya sauko ba.Idan

kuma babu gashin kwata-kwata to sai a shafi fatar kai kuma tilas ne a

shafi fatun kunnuwa.

7. Sannan sai mutum ya wanke kafafuwansa shima sau daya ne ya

wajaba,amma idan akayi sau uku yafi falala.




FA'DAKARWA

1, wuraren da ake yankewa a yayin alwala guda hudu ne.

(a) kurkurar baki da shaka ruwa da wanke fuska.

(b) hannaye

(c) shafar kai da kunnuwa

(d) kafafuwa zuwa idan sawu

2 Tilas ne a wanke wadann gabbai a jere daya-bayan daya,idan kuwa

aka bar wata gabar ba a wanketa ba har jiki ya bushe,to alwala ta

baci,sai a fari wata.

3. An so mutum idan ya kammala alwalarsa yace: "ASH-HADU

ANLAILA'HA ILLALLAHU WA ANNA MUHAMMADAN ABDUHU WA

RASULUHU"

MA'ANA "Na shaida babu abin bauta bisa cancanta sai Allah shi kadai

yake bashi da abokin tarayya,kuma na shaida Annabi Muhammad bawan

Allah ne kuma Manzonsa ne.






KUNGIYAR Atiosa Atiosa TANA SHIRYA WAINNAN ABUBUWAN NE DOMIN ZABURAR DA DALIBANMU.

MUNA ROKON ALLAH YA SANYA MANA ALBARKA MARA IYAKA.


YA KARA TAIMAKONMU CIKIN ABUBUWAN DA MUKA SANYA A GABA.

YA BAMU IKON CIGABA DA GUDANARWA.

Previous
Next Post »

Welcome to ATIOSA Official Website. Atiku Auwal Old Students Association.